Advertisement

Safara’u Ta Bayyana Yadda akayi Bidiyon Ta Na Tsiraici Ya Bayyana har ya Zagaye Duniya

Posted by

Safara’u Ta Bayyana Yadda akayi Bidiyon Ta Na Tsiraici Ya Bayyana har ya Zagaye Duniya

Yadda aka yi bidiyon tsiraicina ya karade duniya – Safara’u

Advertisement

Matashiyar mawakiyar nan a arewacin Najeriya, Safeeya Yusuf, wadda aka fi sani da Safara’u, ta bayyana yadda wani bidiyon tsiraicinta ya karade duniya.

A watannin baya ne bidiyon tsiraicin Safara’u, mai fitowa a shirin Kwana Casa’in da Arewa24 ke shiryawa, ya fita duniya.

Bayan fitar bidiyon, masu shirya fim din sun dakatar da ita daga shirin lamarin da ya sa ta tsunduma cikin harkokin wakoki.

Advertisement

Sai dai wakokin nata suna tayar da kura inda ake ganin suna bata tarbiyya, ko da yake ta ce tana fadakar da jama’a ne.

A wata tattaunawa ta musamman da BBC Hausa, Safara’u ta bayyana yadda aka yi bidiyon ya fita a duniya da kuma wadanda take zargi da fitar da shi.

Matashiyar ta ce ta shiga mawuyacin hali bayan faruwar lamarin inda ta kai har wata uku ba ta fita ko waje ba, har ma ta kai ana jifan ta da duwatsu idan ta zo wucewa ta wani wuri.

Advertisement

Safara’u ta ce an haife ta ne a garin Kano, mahaifinta dan garin Yola, mahaifiyarta kuma ‘yar Jihar Borno inda ta ce zama ne ya kawo su Kano. Ta kuma yi karatu a garin Ibadan na Jihar Oyo, bayan sun dawo Kano kuma sai ta shiga makarantar sakandare.

Wasu sun ce madigo nake yi

Ta bayyana cewa mutane da yawa sun ce tayi abin ne domin tura wa wata kawarta da suke madigo tare inda wasu kuma ke cewa ta aika wa saurayinta bidiyon ne.

‘‘Na kan yi irin wannan bidiyo na ajiye a wayata saboda jin dadi ko na wani abu daban, kuma ni na sani kashi 70 cikin 100 na mata na irin wadannan bidiyo su ajiye a wayoyinsu”, in ji Safara’u.

Ta ce duk da cewa ba ta san wanda ya yada bidiyon ba, amma tana zargin wadanda take tare da su kamar kawayenta saboda tana yawan ba da wayarta ga mutane domin yin kira.

Ta ce dukkan ‘yan uwanta sun ce mata wannan kaddara ne na rayuwa kuma ta dau dangana, amma mutanen gari ke tsinuwa suka yi ta mata da kuma kiranta da sunan karuwa wanda har ta kai ga ta kusan toshe dukkan shafukanta na sada zumunta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *