Anyi Sallar Jana’izar Mutanan Da ‘Yan Bindiga Suka Hallaka Yayin Da Suke Gudanar Da Sallar Juma’a A Zamfara

Posted by

Anyi sallar jana’izar mutanan da wasu ‘yan bindiga suka hallaka yayin da suke gudanar da sallar juma’a a wani kauye dake yankin jihar zamfara state.

Mutanan da aka kashe sun hada da yara sama da kimanin mutum goma tare da iyayen yaran sama da kimanin mutum 20,000 yayin da suke gudanar da sallar juma’a a kauyen nasu.

‘Yan bindigar dai sunyiwa mutanan kawanya, domin ganin koda mutum daya bai tsira daga cikin mutanan ba, haka zalika sun hallaka mutanan yayin da suka tabbatar sun shiga sallar ta juma’a domin ganawa da ubangijin su.

Jami’an tsaron yankin na jihar zamfara sun bayyana afkuwar wannan lamari a daren jiya asabar yayin da suka tabbatar da afkuwar lamarin kafin su bayyanawa duniya faruwar abinda ya kasance a jihar.

Gwamnan jihar matawalle yace, a gaggauta kamowa mutanan da suka aikata wannan laifi domin hukunta su, akan abinda suka aikata akan al’ummar yankin dake kauyen na jihar shi, cewar gwamnan matawalle na zamfara.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *