Shahararren Shugaban ‘Yan Bindiga Bello Turji Da Ya Addabi Mutane Ya Ajiye Makamai Ya Ce A Zauna Lafiya.

Posted by

Shahararren Shugaban ‘Yan Bindiga Bello Turji Da Ya Addabi Mutane Ya Ajiye Makamai Ya Ce A Zauna Lafiya

Shahararren Shugaban ‘Yan Bindiga Bello Turji Da Ya Addabi Mutane Ya Ajiye Makamai Ya Ce A Zauna Lafiya.

Mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Sanata Hassan Nasiha, ya yaba da matakin da Turji ya dauka na gujewa ‘yan bindiga ya kawo zaman lafiya a kananan hukumomi uku da ke fama da munanan hare-haren ‘yan bindiga a jihar.

Ya ce, a cikin makonni biyar da suka gabata, ba a samu wani tashin hankali tsakanin Hausawa da Fulani a kananan hukumomin Shinkafi, Zurmi da Birnin Magaji na jihar ba, saboda tattaunawa dake wakana a tsakanin bangarorin biyu.

A cikin rahoton wanda gidan Talabijin na Channels ya fitar, ya ce kwamitin da gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya kafa, ya gana da sansanonin ‘yan bindiga tara a jihar, inda suka samu jin ta bakin ‘yan fashin.

Da yake jawabi, ya ce a yanzu Turji na hada kai da gwamnatin jihar domin ganin an kawo karshen ‘yan fashi a jihar, da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Zamfara.

Rahoton da ke cewa sarkin ‘yan fashin, Bello Turji, ya rungumi zaman lafiya, ya jawo cece-kuce daga jama’a.

Me zaku ce akan wannan? Ku Saki Jikinku wajen fadin ra’ayoyin ku tare da mu a wannan shafi

https://youtu.be/SHpwmTxDUng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *