Innalillahi wa’inna Ilaihi Raji’un: Kalli yadda ta haihu a hannun Kidnappers

Posted by

Innalillahi wa’inna Ilaihi Raji’un: Kalli yadda ta haihu a hannun Kidnappers

‘Yan Bindiga Sun Saki Matar Shugaban NULGE A Zamfara Da Ta Haihu A Kame

Innalillahi wainna ilaihi raji’un. Masu garkuwa da mutanen sun sake ta ne bayan sun karbi kudi naira miliyan 15 a matsayin kudin fansa.

Ramatu Yunusa, matar shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin Najeriya reshen jihar Zamfara, Sanusi Gusau, wacce ke dauke da cikin watanni tara a lokacin da aka sace ta makonni biyu da suka gabata, ta dauki cikin wata yarinya a lokacin da ake garkuwa da ita.

KALLI YANDA: Abinda Yakamata Kusani Dangane da Siyarda Tsoffin Facebook Pages da akeyi

 

Wadanda suka sace tan sun sake ta bayan karbar kudin fansa Naira miliyan 15. Wani dan’uwa da ya shaida wa jaridar Punch da ya sakaya sunansa, ya ce a halin yanzu mahaifiyar da jaririyar da ta haifa suna jinya a daya daga cikin asibitocin garin Gusau.

Ya ci gaba da shaida wa janzakitv cewa da farko an biya Naira miliyan 10 ne domin neman kudin fansa amma a lokacin da matar ta haifi diya mace sai ‘yan fashin suka ce suna bukatar karin kudi ga jaririn.

Mun biya ‘yan fashin kudin fansa N10m kamar yadda suka bukata, amma a lokacin da suke shirin sako ta, ta haifi yarinya mace, sai suka ce dule sai mun biya ƙarin N5m na jaririn da aka haifa.

“Don haka, bayan tattaunawa mai wahala, ‘yan fashin sun amince da karbar wani kudin N5m a matsayin kudin fansa ga jaririn. “Uwar da jaririn da ta haifa a halin yanzu suna asibiti a nan garin Gusau.”

Janzakitv ke ci gaba da addu’ar Allah ya kara kiyaye mu, Allah ya kawo mana karshen wannan bala’i a Najeriya.

CHECK OTHER RELATED POSTS 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *