- Advertisement -

Masha Allah An sako Wasu Mutun Ukku Daga Cikin Mutanenda ‘Yan Bindiga Suka Sace a Jirgin Kasa Na Kaduna Zuwa Abuja

Posted by

Masha Allah An sako Wasu Mutun Ukku Daga Cikin Mutanenda ‘Yan Bindiga Suka Sace a Jirgin Kasa Na Kaduna Zuwa Abuja

Rahotanni daga jihar Kaduna a arewacin Najeriya sun ce ƴan bindiga sun sake sako mutum uku daga cikin fasinjojin jirgin kasan Abuja-Kaduna.

Wani ɗan uwan ɗaya daga cikin mutanen uku ya tabbatar wa da BBC labarin, inda ya ce an sako su ne a ranar Litinin da rana.

- Advertisement -

DUBA WANNAN: Innalillahi Yanzu-Yanzu: ‘Yan Bindiga Sun Tare Motar KTSTA, Sun Kashe Direban, Sun Tafi Da Fasinjojin

Fasinjojin da aka saka ɗin sun haɗa da maza biyu da mace ɗaya.

- Advertisement -

A lokacin da yake tabbatar wa BBC labarin, ɗan uwan ɗaya daga cikinsu ya ce suna kan hanyar zuwa asibiti don duba lafiyar ɗan uwan nasu.

Sakin nasu na zuwa ne kwana ɗaya bayan da ƴan bindigar suka saki wani bidiyo da ke nuna yadda suke zane maza daga cikin fasinjojin.

Sai dai babu wani cikakken bayani zuwa yanzu kan sharuɗɗan da aka cika kafin sakin nasu.

- Advertisement -

A ranar 28 ga watan Maris ɗin 2022 ne masu tayar da ƙayar baya suka kai wa jirgin ƙasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna hari da daddare.

Kuma tun wannan lokacin, wannan ne karo na biyar da suke sakin fasinjojin da kaɗa-kaɗan.

A yanzu saura da aka sako fasinjoji uku, lissafi ya nuna saura mutum 40 suka rage a hannun ƴan bindigar.

- Advertisement -

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *