Yanzu-yanzu Madagwal ya fito ya karyata rade-radin mutuwarsa dake yawo a social media. Kalli Bidiyon Kaga

Posted by

Yanzu-yanzu Madagwal ya fito ya karyata rade-radin mutuwarsa dake yawo a social media. Kalli Bidiyon Kaga

Tun daren jiya juma’a, wasu da ba a san ko su wanene ba suka fara yada karairayin cewar Allah ya karbi rayuwar Jarumi Madagwal.

Hakan yasa janzakitv ta dukufa wanen binciko sahihancin wannan labari.

Kwatsam sai tayi kicibis da bayanan da shi da kanshi Madagwal din ya fitar yanzu-yanzunnan.

Ga abinda yake cewa:

“Allah kasa mu cika da imani 🤲 dan Allah jama’a mu guji yada jita jita wallahi ni ina nan lafiya ta kalau ko ciwon kai bamba amma na tashi da safe wai ana cewa na mutu wallahi wannan maganar ba gaskiya bace kuma in lokacin mu yayi insha Allah zamu tafi domin MUTUWA tana kan kowa fatan mu shine Allah ka mana KYAKYAWAN karshe Darajar shugaban mu Annabi Muhammadu S.A.W 🤲💚🤲”

Wannan shine jawabin da Jarumi Madagwal ya rubuta da hannunsa yanzu-yanzunnan kuma ya rattafa mata hannu a shafinsa dake facebook.

Domin kallon bidiyon danna wannan:

Masu sauraro da karatu, menene ra’ayinku dangane da masu kirkiran karyan mutuwa a social media domin samun kudi?

Don Allah kuma ayi sharing wannan rahoto domin kawar da wancan karyar da ta bazu akan Jarumi Madagwal.

Sai mun ji ra’ayoyinku a comments.

Daduminsa Gwamna Matawale Ya Dakatar Da Sarkin Da Ya Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *