LABARAI

YANZU YANZUN Jami’ai Ankama Wani Matashi Yanayiwa Qanwarshi Fyade

Wani matashi mai suna Abubakar Hamidu, ya fada komar ’yan sanda a Jihar Gombe kan zargin yi wa kanwarsa fyade.

Matashin mai kimanin shekaru 35 da ke zaune a Unguwar Jauro Abare, ana zarginsa da yin lalata da ’yan uwar tasa har sau biyu a lokuta daban-daban.

- Advertisement -

Da yake gabatar da wanda ake zargin ga manema labarai, Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Gombe, Ishola Babatunde Baba’ita, ya ce wani mai suna Muhammad Hamza ne ya shigar da karar matashin a ranar 19 ga watan Yulin da muke ciki.

Baba’ita ya ce mai shigar da karar wanda ke zaune a Unguwar Kasuwar Mata, ya kai wa ’yan sanda korafin cewa wanda ake zargin ya yi lalata da kanwar tasa ce karon farko a wani gida da ya zama kufai a Unguwar ta Jauro Abare.

- Advertisement -

Kwamishinan ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan, ASP Mahid Mu’azu, ya ce an sake kama matashin karo na biyu yana aikata masha’ar da kanwar tasa a bakin wani tafki.

A cewarsa, da zarar sun kammala bincike za su tura wanda ake zargin zuwa kotu domin ya fuskanci shari’a.

READ ALSO:  Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un; An Tsinci Gawar Mata Da Miji Acikin Gidansu

Mr Kurya

The Name is Kurya An Full Time Blogger | Entrepreneur | Online Promoter| Web Designer | Web/App Developer | Content Writer | Your Number 1 B*D A** Blogger 😏 Follow Us Social Media Below

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Sorry You need to turn off your adblocker to browse on this blog please