Inamatuqar Son Sake Komawa Gidan Tsohon Mijina Sani Danja Inji Tsohuwar Matarshi Mansurah Isah

Posted by

Inamatuqar Son Sake Komawa Gidan Tsohon Mijina Sani Danja Inji Tsohuwar Matarshi Mansurah Isah

Awata Fira Da Akayi Da Tsohuwar Jarumar Shirya Finafinan Hausa Ta Kannywood Waro Jaruma Mansura Isah Ta Bayyanawa Manema Labarai Cewar

“Na fi ku son na koma gidan Sani Danja, amma idan zama ya haramta sai hakuri”- Mansura

Tun bayan fitar labarin rabuwar aurenta da Sani Danja a ranar 27 ga Mayun 2021, a karon farko Jaruma Mansura Isah ta magantu inda ta ce jama’a da ke ta bata shawara kan ta koma gidan uban ‘ya’yanta ba su fita son hakan ba.

Jaruma ta shaida wa majiyar DCL Hausa ta mujallar fim magazine cewa idan zama ya haramta dole a yi hakuri da juna duk da yadda ake son juna.

Mansurah, wadda suka haifi ‘ya’ya huɗu da Sani Danja (mace ɗaya, maza uku), ta ce ko da farko ma abin da ya sa ta sanar da duniya labarin rabuwarsu, ta yi hakan ne domin kada a matsayin ta na fitacciya a gan ta da wani a waje ko ta tsaya da wani a riƙa yi mata kallon tana wasa da aurenta ko kuma ma a ce bata dauki auren da daraja ba.

One comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *