Jaruma Mariya Dadin Kowa ta lashe Gasar sarauniyar kyau Ta Yan Matan kannywood

Posted by

Mariya Dadin Kowa ta lashe Gasar sarauniyar kyau Ta kananun matan masana’antar kannywood masu Tasowa

An baiyana jaruma mariya ta cikin shirin Dadin kowa a matsayin wacce ta lashe gasar sarauniyar kyau ta mata masu tasowa a masana’antar kannywood ta shirya finafinai.

Daman dai akanyi gasar duk shekara sannan a samu wacce ta cinye a wannan karan dai an samu jaruma mariya ta cikin shirin Dadin kowa ta cinye kuma an bata kambu.

Jarumar da bawani finafinai take yiba tafi kwarewa a iya Shirin dadin Kowa wanda Arewa 24 take daukar nauyin haskawa duk karshen sati.

Ta baiyana yadda taji dadi da kuma godewa Allah bisa wannan karamcin da yayi mata tace itafa bata taɓa zaton zatazo ta daya ba amma kuma bisa ikon Allah sai gashi ta tafi da wannan kanbom

Ana ganin dai wannan abun da ake yi acikin kannywood ba dai-dai bane bai dace da addini ba anyi kiranshi da koyi da turowa wato yahudawa tunda ko a kasa ma gaba daya yan kudu ne suke haɗawa inda na wannan shekara aka samu wata yar jihar Kano ta lashe gasar

Sai dai su kuma masana’antar kannywood tace tayine saboda ta karawa mata kaimin gyaran jiki da kula da jikinsu

 

One comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *